SHIN AZUMIN WATAN RAJAB (AZUMIN TSOFAFFI) YA INGANTA A SUNNAH???!!!!

SHIN AZUMIN WATAN RAJAB (AZUMIN TSOFAFFI) YA INGANTA A SUNNAH???!!!!

Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki, tsira da amincin Allah su tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wa Sallam da Alayensa da Sahabbansa gaba daya da wadanda suka biyo bayan su da kyautatawa.
Wannan rubutu ya bi yo bayan wata tambaya da aka mun, akan shin ya halatta yin azumin watan Rajab?!

Wannan yasa na kudurci niyyar yin bayani akan wannan qadiyar, tare da neman taimakon Allah (SWA) da ya aka za mun ya yin wannan binciken da kuma rubutun.

WATAN RAJAB:- Yana daya daga cikin watannin musulunci guda hudu da ake kiran su da watanni masu alfarma (ASH-HURUL HURUM).
Allah (SWA) yak e cewa:-
“LALLAI QIDAYAYYUN WATANNI A WURIN ALLAH (SWA), WATA GOMA SHA BIYU NE A CIKIN LITTAFIN ALLAH, RANAR DA YA HALICCI SAMMAI DA KASSAI, A CIKIN SU AKWAI (WATANNI) HUDU MASU ALFARMA…” Suratul Taubah 36.

Watanni ma su alfarma su ne:-
RAJAB, ZUL QADAH, ZUL HIJJAH DA MUHARRAM.

Imamul Bukhari (4662) da Imam Muslim (1679) sun ruwaito hadisi daga Abi Bakharata (RA), Manzon Allah (SAW) y ace;
“A SHEKARA WATA GOMA SHA BIYU NE, A CIKIN SU AKWAI WATANNI HUDU MASU ALFARMA, UKU DAGA CIKI SUNA JERE; ZULQADAH, ZULHIJJAH DA MUHARRAM, RAJAB KUMA SHINE WANDA YA KE TSAKANIN JUMADA SANI (Watan 6) DA SHA’ABAN (watan 8).

@ An sanya musu watanni ma su alfarma ne saboda dalilai guda biyu;

(1). Haramta yin yaki a cikin su da aka yi, sai dai idan abokanan gaba ne suka fara.
(2). Ai kata mummunan aiki a cikin su, ya fi tsanani sama da sauran watannin.

Da wannan ne Allah (SWA) ya hana aikata sabo a cikin wadannan watannin.
Allah (SWA) y ace: “KA DA KU ZALUNCI KAN KU A CIKIN (wadannan) WATANNIN” Tuaba 36.
Duba Tafsirin Shaikh Nasirus Sa’adi karkashin wannan ayar shafi na (373).

AZUMI A WATAN RAJAB DA MAGANGANUN MALAMAI:-

Babu wani dalili ingatacce day a zo akan yin azumin a watan Rajab, ko hadisi ingatacce dangane da falalar azumi a watan, dukkan hadisan da suka zo hadisai ne na karya da’ifai.

Abu Dauda ya ruwaito hadisi a sunan na shi (2428) dangane da muhimmancin azumi a watanni masu alfarma. Manzon Allah (SAW) y ace: “KA AZUMCI WATANNI MASU ALFARMA…..”
Imam Albani ya Da’ifantar da hadisin a cikin Da’if Abi Dauda.

@ Shaikhul Islam Ibn taimiyyah (RH) y ace: “Ke banta watan rajab da yin azumi, dukkan hadisan da su ka zo akan haka da’ifai ne (masu rauni), bal ma hadisan karya ne, ma’abota ilimi bas a daukan hadisan a bakin komai, domin bas a cikin hadisan da ake amfani das u don nuna falalar aikata abu (Fadha’ilul A’amal), bal dukkan su ma hadisai ne na karya..”
Duba Majmu’u Fatawa (25/290).

@ Imam Ibnul Qaiyim (RH) y ace; “Dukkan hadisin day a ambaci azumin watan rajab da sallatar wasu darare a cikin sa, karya ne kirkirarre”.
Duba Almanarul Muniif (shafi 96).

@ Alhafiz Ibn Hajar Al-Asqalani yak e cewa; “Babu wani abu da aka ruwaito na falalar watan Rajab, ko yin azumi a cikin sa, ko azumtar wasu adadin kwanaki ayyanannu, ko tsayuwar wasu darare kebantattu”.
Duba Tabyinul Ajab (shafi 11).

@ Imam Sayyid Sabiq (RA) yak e cewa; “Azumin watan rajab bas hi da wani fifko na falala akan waninsa cikin watanni, sai dais hi yana daga cikin watanni (guda hudu) ma su alfarma, kuma ba a samu a cikin sunnah ingatacci cewa yin azumi a cikin sa yana da falala kebantacce, abunda ya zo akan haka (ma’ana hadisan da suka zo) ba a kafa hujja das u (domin da’ifai ne)”
Duba Fiqhus-Sunnah (1/383).

@ An tambayi Shakh Salihul Usaimeen (RH) dangane da azumi ranar 27 ga watan rajab da kuma tsayuwar dararen sa.
Sai ya amsa da cewa:
“Yin azumi ranar 27 ga watan Rajab da tsayuwar darensam kebance shi da haka bidi’a ne, dukkan bidi’a kuma bat ace”
Duba Majmu’u fatawa na Usaimeen (20/440).

A takaice da wadannan dalilai da muka ambata za mu fahimci cewa kebance watan Rajab da yin azumi ko nafilfili bai ingantaba a Sunnah.

Don haka mu tsaya a inda Sunnah ta umurce mu akai, mu guji aikata bidi’a.

Allah ya tabbatar da mu akan sunnar Manzon allah (SAW).

Wannan shine a takaice.

Dan uwanku:
Muhammad Albani Misau.
1/7/1436. 20/4/2015

Leave a comment